MAMMAN MANGA II (1886-1900)
Bayan
mutuwan Sarki Sale said dan sa Mamman manga II ya gaje shi. Ya mulki Misau na
shekaru 14. Mamman mutum ne mai basira, ilimi da shugaba mai hikima. Yana da
zafi a gudanar da mulki. Baya barin bawa ko kowani mutum ya gudu a wajen yaki.
Sarkin ya kuma ci nasaran ciwo yankunan Diri, Yanda Kulus, Gabukka, Takai da
Fika. Wannan ya fadada masaratar sosai. A 1990 ya ziyarci surukin sa sarkin
Kano Aliyu wanda a hanyar sa ta dawowa Misau ya mutu a Dafo.
AHMADU II (1900 – 1993)
Sarki Ahmadu
II kanin Sarki Manga II ne, yayi mulki na shekaru biyu da watanni 9. Lokacin
daya tabbatar turawan mulkin mallaka zasu zo su hambarar da mulkin sa, maimakon
ya bari su iso su zubar masa da daraja
sai ya yanke shawaran barin Misau ranar 8th
December, 1902. Bayan kwanaki 29 da barin sa sai ya yanke shawaran juyowa gida.
Dawowan sa sai ya riske dan uwan sa Alhaji Tafida ya rufe masa kofofin ganuwa.
Alhaji tafida yana fatan kalifa zai cire Ahmadu a sarki ya nada shi.
Sarki Ahmadu
ya hada sojojin sa yayi wa Misau kawanya na watanni hudu, har April 1903, zuwa
lokacin da tsohon Kalifan sokoto, Kalifa Attahiru ya gudu ma turwan burtaniya
ya samu Sarki Ahmadu II a wajen ganuwar Misau ya dauke shi suka tafi tare zuwa
Burmi.
Bayan anci
Attahiru da yaki an kashe shi, Sarki
Ahmadu ya gudu zuwa wajejen Makka. Shi da mutanen sa daga baya suka sauka kusa
da kogin Nile a kasar Sudan.
SARKI ALHAJI (1993 – 26)
Bayan guduwan
sarki Ahmadu sai turawan Birtaniya suka maida kanin sa Alhaji a matsayin sarki
a 1903. An ce gudumawar daya bama baturen burtaniya mai kula da yankin Bauchi
Mr. C.L. Temple wajen kama mutanen Sarki Ahmadu a Nafada ya taimaka wajen bashi
sarauta.
Turawa sun
saka Misau karkashin Katagum, amma daga baya an dawo mata da yancin ta a
matsayin masarauta mai zaman kan ta karkashin kasar kano. A 1915 an fadada
masarautar tare da kara Dambam da Jalam a karkashin masarautar Misau. A dukkan
Lokacin Sarki Alhaji yayi kokari wajen karfafa addnin musulunci a masarautar sa
duk da matsin lamba daga turawa. A lokaci guda kuma, an samu bunkasan noma da
kasuwanci a zamanin sa, watakila ma saboda ci gaban da sarki ya kawo yasa King
George V na England a 26th February 1921 ya bama sarki Alhaji lambar
Yabo Medal for African Chiefs. Alhaji Tafida ya mutu ranar juma’a 27th
September, 1926.
SARKI AHMADU III (1927 – 1979)
Bayan
mutuwan ubansa sai sarki Ahmadu III ya dare karagar mulki daga kujerar sa ta
waziri. Sai aka maida Misau Emirate Bauchi province daga Kano province. Sarkin,
sarkin gargajiya kuma malamin addini, ya dawo da sunan sarautar sarkin bornu ta
gabas wanda sarkin Misau Mamman Manga I ya gada. Ya karbi mulki da kuruciya yana
dan shekaru 26 kuma mai ilimi, tsayayye a dukkan matsalolin mulki.
Misau ta ga
ci gaba a zamanin sa, ya bada muhimmaci wajen gina makarantun boko tare da
islamiyoyi. An nada emirate council lokacin sa, kawo modern agricultural
production, postal agency, wutar lantarki, Misau general hospital duk a lokacin
sa aka samar dasu. Ya fi kowa dadewa a gadon mulki da shekaru 53. Ya rasu a
1979.
SARKI MUHAMMADU MANGA III (1979 – 2015)
Sarki na 10,
ya gaji baban sa. An haife shi 7th September, 1937. Muhammadu Manga
kamar kowane sarki ya tashi cikin ilimi. Yayi karatun kura’ani a wajen limamin
gari har zuwa 1948 lokacin daya shiga Misau Elementary School. Daga nan ya wuce
sannaniyar Bauchi Midle School. Neman ilimin sa ya kaishi har Insititute of
Administration, Ahmadu BelloUniversity, Zaria Karin course kan sha’anin mulki. Anan ya koyi ilimi wanda zai zaunar dashi
cikin shirin zama sarki.
Bayan
dawowan sa daga Bauchi Middle school aka bashi Secretary to the emirate
council, Misau Native Authority a 1955. A 1958 aka nada shi Hakimin Misau –
Yarima. Mukamin da ya rike shekaru 21.
A October 30th,
1979 aka nada shi sarkin Misau na 10
tare da bashi Second Class of Office a 1980. A kasa da shekaru biyu da hawan sa
mulki gwamnatin jihar Bauchi taga ya cancanci a maida Emirate din First class
status a July 1982.
An samu
gagarumin ci gaba a lokacin Manga III. An mayar da Misau Urban Centre bayan
State Urban Development Board tayi nazari. Wannan yasa aka sanya Misau akan
main National Grid na wutar lantarki, tare da yin hanyoyi irin na birane da
tsara gari akan tsarin birni.
Wasu ci
gaban sun hada da kafa cibiyar karatun Islama, A.D Rufa’i college for Legal and
Islamic Studies, tare da kawo local government cikin masarautar.
A shekaru
Alhaji Muhammadu Manga ya karbi lambar yabo da sandunan girmamawa kadan daga
ciki; fellowship of administration Management of Nigeria (FIAMN), Lagos;
Development in Nigeria Merit Award (DINMA). Sauran sun hada da NEMLA, CDTA, da
kuma Honorary Doctorate Degree in Mangament and public Administration from
Atlas University, Okija, a Anambra State.
Mafi
muhimmaci shine award of the Nigeria National Honors na OON a may 2009.
Sarki
Muhammad Manga III ya rasu a August 2015 bayan fama da rashin lapia.
No comments:
Post a Comment