FULATA BORNO
Gwani
mukhtar an haife shi a 1738 a wani gari Gurno. Yayi karatun Arabi da addinin Musulunci
a wajen wani malami Gwani Lawal a Wuro Bokki. Ya auri yar malamin sa da ake
kira Asta. Da mallam Lawal ya mutu sai Gwani Mukhtar ya zama sarkin da kuma
limami a wuro bokki.
Imam Gwani
Muktar hazikin shugaba ne, mai hakuri, takawa, gaskiya, da kuma adalci. Yayi
yake-yake inda ya dinga cin kauyukan kusa da yaki yana musuluntar dasu.
Tarihin Gwani Mukhtar na farko tarihin Bornu ne bana Misau ba. Lokacin da Imam Gwani Muktar yaji labarin Shehu Usman Danfodio a Saifawa sai ya kai masa Ziyaran Mubayi’a a shekaran 1806, ya kuma juya baya a Sarkin Borno, Mai Dunama, saboda su akwai shirka a cikin musuluncin su. Shehu Usman ya bashi tuta domin ya fita jihadi.daga nan sai ya zabura ya fara yakan garuruwan da suke makwabtaka wadanda bana musulmai ba yana cin su da yaki. Da sarkin Bornu Mai Dunama yaji labari sai ya aika masa da Madakin sa, Gangarama, zuwa gujba ya yaki Mujaddadi Gwani Muktar, amma Mujaddadi Gwani Muktar ya shi da yaki. Sai karfin mulkin Gwani Mukhtar ya kara tasiri, yaci gaba da yaki yana cin garuruwa yana musuluntar das u. Ya nufi gabashi da yaki yana tafiya ba tare da hamayya ba har ya iso birnin Ngazargamu, Babban birni, fadan masarautar Bornu, Yaci garin da yaki bayan an kwafsa yakin kwana biyu kadai. Ya samu nasaran kama Ngazargamu ranan 12th March, 1808.
Tarihin Gwani Mukhtar na farko tarihin Bornu ne bana Misau ba. Lokacin da Imam Gwani Muktar yaji labarin Shehu Usman Danfodio a Saifawa sai ya kai masa Ziyaran Mubayi’a a shekaran 1806, ya kuma juya baya a Sarkin Borno, Mai Dunama, saboda su akwai shirka a cikin musuluncin su. Shehu Usman ya bashi tuta domin ya fita jihadi.daga nan sai ya zabura ya fara yakan garuruwan da suke makwabtaka wadanda bana musulmai ba yana cin su da yaki. Da sarkin Bornu Mai Dunama yaji labari sai ya aika masa da Madakin sa, Gangarama, zuwa gujba ya yaki Mujaddadi Gwani Muktar, amma Mujaddadi Gwani Muktar ya shi da yaki. Sai karfin mulkin Gwani Mukhtar ya kara tasiri, yaci gaba da yaki yana cin garuruwa yana musuluntar das u. Ya nufi gabashi da yaki yana tafiya ba tare da hamayya ba har ya iso birnin Ngazargamu, Babban birni, fadan masarautar Bornu, Yaci garin da yaki bayan an kwafsa yakin kwana biyu kadai. Ya samu nasaran kama Ngazargamu ranan 12th March, 1808.
Mujaddadi Gwani
Muktar ya aika babban dan sa Mahammadu Manga ya kai ma mujaddadi shehu usman
danfodio labari na aiki mai kyau na jihadi da suke yi shi kuma ya zauna a
Ngazargamu na wata bakwai har zuwa lokacin daya karbi order daga shehu usman
danfodio ya koma gida. Akan hanyar sa ta komawa gida ne sarkin bornu ya bishi
ya kashe shi a watan November 1809. Aka aika dan gwani mukhar Mamman Manga ya
tafi da labari ya gaya ma Mujaddi. Shehu ya bama Mamman Tuta a matsayin sarkin
Fulata-Borno.
Duk da cewa
tushen yan Misau ya samo asali ne daga Bornu, daga wannan lokacin iyi gaba sai
harkokin mulkin su ya koma sokoto.
Amma bayan
kashe Gwani Muktar sai mutanen Mai Dunama (Bare-bari) suka gudu Birnin Kabella.
Bada jimawa ba sai Mamman Manga tare da Mallam Zaki, Sarkin Katagum da Buba
Yero, Sarkin Gombe suka kai hari a Birnin Kabella suka ci mutanen Bornu da yaki.
Mallam zaki ya ikirarin kasar arewa da Bornu, Buba Yero kasar kudu da bornu
sabida taimaka masa a wajen yaki da sukayi. Manga yaki basu kasashen da suka
bukata saboda haka suka dawo gida shi kuma ya zauna a bornu.
A daidai
wannan lokaci sai Laminu yazo wajen sarkin Bornu Mai Dunama ya masa tayin
taimako idan zai bashi kasar da zai zauna a karkashin Bornu. Mai Dunama ya
amince sai suka hada karfi suka kori manga zuwa yammacin Gujba. Haka dai suka
ci gaba da fada na tsawon shekaru.
Bayan Mamman
Manga ya zauna a Gujba na watanni biyar sai ya gina garin kan sa, Damaturu,
arewa da Gujba kadan. Anan ne kanin Manga, Aliyu, ya kai kukan Mamman sokoto
cewa mutane sun gaji da rashin iya mulki na yayan sa kuma sun fi kaunan sa ya
zama sarki akan yayan sa Mamman. Kalifa yayi kokari ya kwantar da hankali sai
ya aika wazirin sa, wazirin sokoto Gidado, ya tumbuke Mamman ya nada kanin sa
Aliyu sarki. Duk fulanin garin suka bar Damaturu zuwa gudun hijira tare da Mamman
Lapia a bornu, suka bar Kanuri kawai tare da Aliyu a Damaturu. Da kalifa yaji
haka sai ya order a mayar da Mamman matsayin san a Sarki.
Daga
damaturu sai mamman yayi gabar, amma Shehu Laminu ya kore shi zuwa yankin
Bauchi. Yakubun Bauchi ya bashi kasa ya zauna a Buri-Buri, daga nan kuma ya
dauke shi suka tafi ziyara sokoto.
A sokoto ne
aka umurci Yakubu ya yaki Bornu. Bayan Yakubu yayi nasaran ceto Fulani daga
tsoron hare-hare na Kanuri bayan sun ci Al-Kanemi da yaki a shekaran 1827, sai
yakubu ya hada hannu da Dan Kauwa na Katagum aka kama Misau aka kori mazauna
cikin ta a shekaran 1827.
Husuma sai
ta kaure tsakanin sarakuna Yakubun Bauchi da Dan Kauwa na Katagum akan mai
mallakan Misau, Mamman Manga ya maida jawabi a kalifa Bello, Kalifa ya umurci
Yakubu ya maida kasan Misau hannun Mamman Manga, dan Gwani Muktar. Da haka ne
Mamman Manga ya zama Sarkin Borno ta Gabas.
A haka manga
ya zama sarkin Misau na farko. Amma rundunar Manga ta waste saboda shekara da
shekaru na gwabza yaki, sai akayi yarjejeniya zasu bishi Misau ko kuma su dinga
aika haraji.
Mamman manga
ya mulki Misau na shekaru biyu har zuwa mutuwar sa a 1833 shekarun sa 57 a
duniya.
AHMADU (1833 - 1850)
Imam Ahmadu,
Da ga Mujaddadi Gwani Muktar, dan uwan Mamman Manga, ya gaji dan uwan sa
Mamman. Ya mulki Misau shekaru 17. A
lokacin sa ne aka gina ganuwa, aka kuma gina fadan masarautar Misau. Yayi
yake-yake ya ci garuruwa da dama. Ya kai hari ma Tangale fiye das au goma ba
tare da nasara ba, a Bornu ma ba nasara (saboda ya rama kasha uban sa Gwani
Muktar). Watakila babban ci gaban da
Sarki Ahmadu na farko ya kawo lokacin sa shine fadadan addinin musulunci. ya
gina masallatai da islamiyoyi. Ahmadu yayi rashin lapia ya mutu a 1849.
USMAN (1850 - 1861)
Bayan
mutuwar Sarki Ahmadu I sai baffan sa (Dan Mamman Manga ne), Usman ya gaje shi.
Mayaki mai hidima a addini, Usman, kamar kakannin sa yaci gaba da jihadi. Cikin
wadanda yaci da yaki akwai Ma’aniya, Dawa, Tikau da Busongo, sauran sune Iubbi
da Kwararrafa a Benue.
A 1855
sarkin gombe kwairanga ya roki Sarki Usman ya taya shi yaki da Tangale. Amma an
ci su da yaki. Hakanan a yakin Numan ma sun sha kashi tare da rasa mayaka da
yawa.
A cikin gida
Usman ya hadu da tawaye. An zarge shi da jawo nasa jiki kawai da Koran wanda ba
nasa ba. Yayi mulki shekaru 11 ance kuma sokoto ne suka tumbuke shi a 1861.
Masana tarihin Misau sun ce Sale ne ya masa juyin mulki lokacin baya nan yana
taya sokoto yaki. Usman ya mutu a gudun hijira a Yelwa, kusa da Bauchi shekara
bayan tumbuke shi.
SARKI SALE (1861-86)
Sarki Sale,
brother ga sarkiUsman, yayi mulki tsawon shekaru 25. Yayi suna akan yakuna daya
ciwo. Yana da mayaka masu masa biyayya. Ance yayi nasarori a yakuna akalla 72.
Wasu daga cikin mashahuran yankunan daya kama; maguzawan Wazalenga, Wazza,
Kubbi, Waja Talessa a Jihar Gombe. Kare-karen Jalam da Zumbuk da Gala a yankin
Warji. Ba mamaki dokin sa – Wauaro har yanzu ana tuna shi. Sale mutum ne mai
hazikanci a harkan addini. An kashe shi a yakin Ningawa a Tangali a 1886
shekarun sa 72.
Akwai wayanda suka ruwaita cewa gwani MUKHTAR yanada da Mai suna inrahima Wanda yayi rayuwa tare da sarkin musulmi muhd bello ya auri daya daga cikin kannesa Wanda ya haifi da Mai suna islmail. Sannan Muna son silailar shajara din gwani MUKHTAR inda wasu cikin zuriyarsa suke jinginashi dasharifta wasu kuma suke korewa menene gaskiyar maganar?
ReplyDelete